6 Ubangiji kuwa ya dakatar da nufinsa, ya ce,“Wannan ma ba zai faru ba.”
7 Ubangiji kuma ya nuna mini wani wahayi. A wahayin sai na gan shi, yana tsaye kusa da bangon da ake ginawa. Yana riƙe da igiyar awon gini.
8 Ya tambaye ni, ya ce, “Amos, me ka gani?”Sai na ce, “Igiyar awon gini na gani.”Ya kuma ce,“Duba, da wannan zan nuna yaddajama'ata sun zama kamar bangonda ya karkace.Ba zan sāke nufina a kan yi musuhukunci ba.
9 Zan hallakar da wuraren sujada nazuriyar Ishaku.Za a hallakar da tsarkakan wurare naIsra'ila.Zan fāɗa wa zuriyar sarkiYerobowam da yaƙi.”
10 Amaziya, firist, na Betel kuwa, ya tafi ya faɗa wa Yerobowam Sarkin Isra'ila, ya ce, “Amos yana shirya maka maƙarƙashiya a cikin jama'ar Isra'ila. Maganganunsa za su hallakar da ƙasar.
11 Abin da ya faɗa ke nan, ‘Za a kashe Yerobowam a bakin dāga, a sa jama'ar Isra'ila su yi ƙaura zuwa wata ƙasa.’ ”
12 Amaziya kuwa ya ce wa Amos, “Kai maƙaryaci ne na ainihi! Koma ƙasar Yahuza ka nemi abin zaman gari, ka yi ta annabcinka a can.