1 Ubangiji ya nuna mini wahayi, sai na ga kwandon ɓaure na ci.
2 Sai Ubangiji ya ce, “Amos, me ka gani?”Na ce, “Kwandon ɓaure na ci.”Ubangiji kuma ya ce mini, “Ƙarshen jama'ata Isra'ila ya zo. Ba zan sāke nufina a kan yi musu hukunci ba.
3 Waƙoƙin da akan raira a fāda, za su zama na makoki a wannan rana. Za a iske gawawwaki ko'ina. Ba za a ji motsin kome ba.”
4 Ku ji wannan, ku da kuke tattake masu bukata, kuna ƙoƙari ku hallakar da matalautan ƙasar.
5 Kuna ce wa kanku, “Mun ƙosakeɓaɓɓun kwanakin nan su wuce,Mu sami damar yin kasuwancinmu.Yaushe Asabar ɗin za ta ƙare ne?Ko mā sami damar kai hatsinmukasuwa,Mu sayar musu da tsada,Mu yi awo da ma'aunin zalunci,Mu daidaita ma'auni yadda za mucuci mai saya?
6 Za mu sayi matalauci da azurfa yazama bawa,Mai fatara kuma da takalmabi-shanu.Za mu sayar da ruɓaɓɓen hatsi,Mu ci riba mai yawa.”
7 Ubangiji Allahn Isra'ila ya riga yarantse,Ya ce, “Ba zan manta da mugayenayyukanku ba.