15 “Ka ɗauka a ranka ka bi gurbin da mugaye suke bi kullum?
16 Kafin ma su kai ga kwanakinsu,Sai rigyawa ta shafe su.
17 Su ne mutanen da suka ƙi Allah,Suka kuwa gaskata ba shi da ikon yi musu kome,
18 Ko da yake Allah ne ya arzuta su.Ba na iya gane tunanin mugaye.
19 Mutanen kirki suna murna,Marasa laifi kuma suna dariyaSa'ad da suka ga ana hukunta mugaye.
20 Duk abin da mugu ya mallaka ya hallaka,Wuta kuwa ta lashe kowane abu da ya ragu.
21 “Yanzu fa, Ayuba, sai ka yi sulhu da Allah,Ka daina ɗaukarsa kamar maƙiyinka,In ka yi haka, to, za ka sami albarka.