21 “Yanzu fa, Ayuba, sai ka yi sulhu da Allah,Ka daina ɗaukarsa kamar maƙiyinka,In ka yi haka, to, za ka sami albarka.
22 Ka karɓi koyarwar da yake yi,Ka riƙe kalmominsa a zuciyarka.
23 Hakika sai ka yi tawali'u, ka koma wurin Allah,Ka kawar da dukan muguntar da ake yi a gidanka.
24 Ka jefar da zinariyarka, zinariyarka mafi kyau,Ka jefar da ita kamar dutse ko ƙura.
25 Bari Allah Mai Iko Dukka ya zama zinariyarka,Ya zama azurfa, wadda aka tula dominka.
26 Sa'an nan za ka dogara ga Allah kullayaumin,Ka kuma tarar shi ne asalin farin cikinka.
27 Sa'ad da ka yi addu'a zai amsa maka,Za ka kuwa kiyaye alkawaran da ka yi.