11 “Na yi ta dubawa saboda manya manyan maganganun fariya da ƙahon yake hurtawa, sai na ga an kashe dabbar, an jefar da gawar cikin wuta don ta ƙone.
12 Sauran dabbobi kuwa aka karɓe mulkinsu, amma aka bar su da rai har wani ƙayyadadden lokaci.
13 “A cikin wahayi na dare, na ga wani kamar Ɗan Mutum.Yana zuwa cikin gizagizai,Ya zo wurin wanda yake Tun Fil Azal,Aka kai shi gabansa.
14 Aka kuwa danƙa masa mulki, da ɗaukaka, da sarauta,Domin dukan jama'a, da al'ummai, da harsuna su bauta masa.Mulkinsa, madawwamin mulki ne,Wanda ba zai ƙare ba.Sarautarsa ba ta tuɓuwa.”
15 “Amma ni Daniyel raina ya damu, wahayin da na gani ya tsorata ni.
16 Sai na matsa kusa da ɗaya daga cikin waɗanda suke tsaye a wurin, na tambaye shi ma'anar waɗannan abubuwa duka. Sai ya bayyana mini, ya kuma ganar da ni ma'anar waɗannan abubuwa.
17 Waɗannan manyan dabbobi guda huɗu, sarakuna ne huɗu waɗanda za su taso a duniya.