1 A sa'ad da Allah ya fara halittar Sama da duniya,
2 duniya ba ta da siffa, sarari ce kawai, duhu kuwa yana lulluɓe da fuskar zurfin teku, Ruhun Allah kuma yana shawagi bisa ruwayen.
3 Allah ya ce, “Bari haske ya kasance,” sai kuwa ya kasance.
4 Allah ya ga hasken yana da kyau. Allah ya raba tsakanin hasken da duhu,