8 Kush ya haifi Lamirudu, shi ne mutumin da ya fara ƙasaita cikin duniya.
9 Shi riƙaƙƙen maharbi ne a gaban Ubangiji, domin haka akan ce, “Shi kamar Lamirudu ne riƙaƙƙen maharbi ne a gaban Ubangiji.”
10 Farkon inda ya kafa mulkinsa a Babila, da Erek, da Akkad, da Kalne ne, dukansu a ƙasar Shinar suke.
11 Daga wannan ƙasa ya tafi Assuriya ya gina Nineba da Rehobot-ir, da Kala,
12 da Resen wadda take tsakanin Nineba da Kala, wato babban birni.
13 Mizrayim shi ne mahaifin Ludawa, da Anamawa, da Lehabawa, da Neftuhawa,
14 da Fatrusawa, da Kasluhawa (inda Filistiyawa suka fito) da kuma Kaftorawa.