1 Saratu ta yi shekara ɗari da ashirin da bakwai a duniya,
2 sa an nan ta rasu a Kiriyat-arba, wato Hebron, a ƙasar Kan'ana. Ibrahim kuwa ya tafi ya yi makoki, yana baƙin ciki domin Saratu.
3 Ibrahim ya bar gawar matarsa, ya je ya ce wa Hittiyawa,
4 “Ni baƙo ne, ina tsakaninku, ina zaman baƙunci. Ku sayar mini da wurin yin makabarta, domin in binne matata, in daina ganinta!”
5 Hittiyawa suka amsa wa Ibrahim suka ce,