2 A can, sai Yahuza ya ga 'yar wani Bakan'ane mai suna Shuwa. Ya aure ta, ya shiga wurinta,
3 ta yi ciki, ta haifi ɗa namiji, ya kuwa raɗa masa suna Er.
4 Sai ta sāke yin ciki, ta kuma haifi ɗa, ta raɗa masa suna Onan.
5 Har yanzu kuma ta sāke haihuwar ɗa, ta raɗa masa suna Shela. A Kezib ta haifi Shela.
6 Yahuza kuwa ya auro wa ɗan farinsa, Er, mata, sunanta Tamar.
7 Amma Er, ɗan farin Yahuza mugu ne a gaban Ubangiji. Sai Ubangiji ya kashe shi.
8 Sa'an nan Yahuza ya ce wa, Onan, “Shiga wurin matar ɗan'uwanka, ka yi mata wajibin ɗan'uwan miji, ka samar wa ɗan'uwanka zuriya.”