20 Sai ramammun, munanan shanun suka cinye shanun nan bakwai masu ƙiba na farko,
21 amma da suka haɗiye su, ba wanda zai iya sani sun haɗiye su, gama suna nan a ramammunsu kamar yadda suke a dā. Sai na farka.
22 Har yanzu kuma, a cikin mafarkina ga zangarku masu kauri kyawawa guda bakwai, suna girma a kara guda,
23 zangarku bakwai kuma busassu sirara waɗanda iskar gabas ta ƙeƙasar, suka fito a bayansu.
24 Siraran zangarkun kuwa suka haɗiye zangarkun nan bakwai kyawawa masu kauri. Na faɗa wa bokaye, amma ba wanda ya iya yi mini fassararsa.”
25 Yusufu ya ce wa Fir'auna, “Mafarkin Fir'auna ɗaya ne, Allah ya bayyana wa Fir'auna abin da yake shirin aikatawa.
26 Waɗannan shanu bakwai, shekaru bakwai ne, kyawawan zangarkun nan bakwai kuma shekaru bakwai ne, mafarkin ɗaya ne.