2 “Faɗa wa Isra'ilawa su karɓo mini kaya daga dukan wanda ya yi niyyar bayarwa.
3 Ga irin sadakokin da za ku karɓa, zinariya, da azurfa, da tagulla,
4 da ulu mai launin shuɗi, da mai launin shunayya, da mai launin ja, da lilin mai laushi, da gashin akuya,
5 da jemammun fatun raguna, da fatun awaki, da itacen ƙirya,
6 da mai domin fitila, da kayan yaji domin man keɓewa, da turaren ƙonawa,
7 da onis, da duwatsun da za a mammanne a falmaran da ƙyallen maƙalawa a ƙirji.
8 Za su yi tsattsarkan wuri domina, don in zauna tare da su.