1 Ubangiji kuma ya ce wa Musa,
2 “Ga shi, na zaɓi Bezalel ɗan Uri, ɗan Hur, na kabilar Yahuza.
3 Na cika shi da Ruhuna, da hikima, da basira, da ilimi, da fasaha,
4 don ya yi fasalin abubuwa na zinariya, da azurfa, da tagulla,
5 da yankan duwatsu masu tamani na jerawa, da sassaƙa itace, da kowane irin aikin fasaha.