8 “Dawakansu sun fi damisa sauri,Sun fi kyarketan maraice zafin hali,Sojojin dawakansu suna zuwa a guje.Sojojin dawakansu suna zuwa daga nesa,Sukan tashi kamar gaggafa da sauri don su cinye.
9 “Sun zo don su yi kama-karya.Ana jin tsoronsu tun ma kafin su zo.Sun tattara bayi kamar yashi.
10 Sukan yi wa sarakuna ba'a,Sukan mai da masu mulki abin wasa.Kowace kagara abin dariya ce a wurinsu,Sukan tsiba ƙasa, su hau, su cinye ta.
11 Sukan wuce da sauri kamar iska,Su yi tafiyarsu.Su masu laifi ne,Ƙarfinsu shi ne gunkinsu.”
12 Ba kai ne madawwami ba?Ya Ubangiji Allahna Mai Tsarki.Ba za mu mutu ba.Ya Ubangiji, kai ne ka sa su su yi hukunci,Ya dutse, kai ne ka kafa su don su yi horo.
13 Kai mai tsarki ne,Ka fi ƙarfin ka dubi mugunta.Kai da ba ka duban laifi.Me ya sa kake duban marasa imani?Kana iya shiru sa'ad da mugu yake haɗiyeMutumin da ya fi shi adalci?
14 Gama ka mai da mutane kamar kifaye a cikin teku,Kamar abubuwa masu rarrafe da ba su da shugaba.