6 Zan cece ka, da wannan birni na Urushalima, daga Sarkin Assuriya, zan ci gaba da kiyaye birnin.”
7 Ishaya ya ce wa Hezekiya, “Ubangiji zai nuna maka alama da za ta tabbatar maka zai cika alkawarinsa.
8 Ubangiji zai komar da inuwa baya da taki goma, bisa ga ma'aunin rana na sarki Ahaz.” Inuwa kuwa ta koma da baya daga fuskar rana har mataki goma.
9 Bayan da Hezekiya ya warke daga rashin lafiyarsa, sai ya rubuta wannan waƙar yabo.
10 Na zaci a gaɓar ƙarfinaZan tafi lahira,Ba zan ƙara rayuwa ba.
11 Na zaci ba zan ƙara ganin Ubangiji baA wannan duniya ta masu rai,Ko kuwa in ga wani mutum mai rai.
12 An datse raina, ya ƙare,Kamar alfarwar da aka kwance,Kamar saƙar da aka yanke,Na zaci Allah zai kashe ni.