11 Zai lura da garkensa kamar yadda makiyayi suke yi,Zai tattara 'yan raguna wuri ɗaya,Zai ɗauke su ya rungume su,A hankali zai bi da iyayensu.
12 Akwai wanda zai iya auna teku da tafin hannu,Ko sararin sama da tafin hannunsa?Akwai wanda zai iya tallabe turɓayar duniya a cikin finjali,Ko ya iya auna duwatsu da tuddai a ma'auni?
13 Akwai wanda zai iya umartar Ubangiji ya yi abu?Wa zai iya koya wa Ubangiji, ko ya yi masa shawara?
14 Da wa Allah yake yin shawaraDomin ya sani, ya kuma fahimta,Ya kuma koyi yadda za a yi abubuwa?
15 Al'ummai ba kome ba ne a wurin Ubangiji,Ba su fi ɗigon ruwa ba,Manisantan tsibirai ba su fi ƙura nauyi ba.
16 Dukan dabbobin da yake a jejin LebanonBa su isa hadaya guda ga Allahnmu ba,Itatuwan jejin kuma ba su isa a hura wuta da su ba.
17 Al'ummai ba kome ba ne ko kaɗan a gare shi.