17 “Su waɗanda za su sāke gina ki suna tafe yanzu,Waɗanda suka lalatar da ke kuwa za su tashi.
18 Ki dudduba, ki ɗaga idonki, ki ga abin da yake faruwa!Mutanenki suna tattaruwa suna komowa gida!Hakika, da yake ni ne Allah Mai Rai,Za ki yi fāriya da mutanenki,Kamar yadda amarya take fāriya da kayan adonta!
19 “Aka lalatar da ƙasar, ta zama kufai,Amma yanzu za ta yi wa waɗanda suke komowa domin su zauna cikinta kaɗan.Waɗanda suka lalatar da ke kuwa,Za a kawar da su daga gare ki.
20 Mutanenki da aka haifa a lokacin zaman talala,Wata rana za su ce miki,‘Wannan ƙasa ta yi kaɗan ƙwarai,Muna bukatar ƙarin wurin zama!’
21 Sa'an nan za ki ce wa kanki,‘Wa ya haifa mini waɗannan 'ya'ya?Na rasa 'ya'yana, ba kuwa zan iya haifar waɗansu ba.Aka kore ni, aka yi mini ɗaurin talala,Wane ne ya haifi waɗannan 'ya'ya?Aka bar ni, ni kaɗai,Daga ina waɗannan 'ya'ya suka fito?’ ”
22 Ubangiji Allah ya ce wa jama'arsa,“Zan nuna alama ga al'ummai,Za su kuwa kawo 'ya'yanku gida.
23 Sarakuna za su zama kamar iyaye a gare ku,Sarauniyoyi za su yi renonku kamar uwaye.Za su rusuna har ƙasa su ba ku girma,Da tawali'u za su nuna muku bangirma.Sa'an nan za ku sani ni ne Ubangiji,Dukan mai jiran taimakon Ubangiji, ransa ba zai ɓaci ba.”