20 Mutanenki da aka haifa a lokacin zaman talala,Wata rana za su ce miki,‘Wannan ƙasa ta yi kaɗan ƙwarai,Muna bukatar ƙarin wurin zama!’
21 Sa'an nan za ki ce wa kanki,‘Wa ya haifa mini waɗannan 'ya'ya?Na rasa 'ya'yana, ba kuwa zan iya haifar waɗansu ba.Aka kore ni, aka yi mini ɗaurin talala,Wane ne ya haifi waɗannan 'ya'ya?Aka bar ni, ni kaɗai,Daga ina waɗannan 'ya'ya suka fito?’ ”
22 Ubangiji Allah ya ce wa jama'arsa,“Zan nuna alama ga al'ummai,Za su kuwa kawo 'ya'yanku gida.
23 Sarakuna za su zama kamar iyaye a gare ku,Sarauniyoyi za su yi renonku kamar uwaye.Za su rusuna har ƙasa su ba ku girma,Da tawali'u za su nuna muku bangirma.Sa'an nan za ku sani ni ne Ubangiji,Dukan mai jiran taimakon Ubangiji, ransa ba zai ɓaci ba.”
24 Kuna iya ku ƙwace wa sojoji wason da suka yi?Kuna iya kuɓutar da 'yan kurkuku daga ɗaurin masu baƙin mulki?
25 Ubangiji ya amsa ya ce,“Wannan shi ne ainihin abin da zai faru.Za a ƙwace kamammun yaƙi,Za a kuma ƙwace wason da masu baƙin mulki ya yi.Zan yi yaƙi da dukan wanda yake yaƙi da ku,Zan kuwa kuɓutar da 'ya'yanku.
26 Zan sa masu zaluntarku su karkashe juna,Za su yi māye, da kisankai, da fushi.Sa'an nan dukan 'yan adam za su sani, ni ne Ubangiji,Wanda ya cece ku, ya fanshe ku.Za su sani ni ne Allah Mai Iko Dukka na Isra'ila.”