14 Adalci da gaskiya za su ƙarfafa ki.Za ki tsira daga shan zalunci da razana.Gama ba za su kusace ki ba.
15 Idan wani ya far miki,Ya yi ne ba da yardata ba,Dukan wanda ya hau ki da yaƙi zai fāɗi!
16 “Ni ne na halicci maƙeriWanda ya zuga wuta ya kuwa ƙera makamai.Ni ne kuma na halicci mayaƙiWanda yakan mori makamai domin kisa.
17 Amma ba makamin da aka ƙera da ya isa ya cuce ki,Za ki iya amsa wa dukan waɗanda za su yi ƙararki.Zan kāre bayina,In kuwa ba su nasara.”Ubangiji ne ya faɗa.