8 Waɗannan jiragen ruwa fa? Suna tafe kamar gizagizai,Kamar kurciyoyi suna komowa gida.
9 Jiragen ruwa ne suke zuwa daga manisantan ƙasashe,Suna kawo mutanen Allah gida.Suna tafe da azurfa da zinariya,Domin su girmama sunan Ubangiji,Allah Mai Tsarki na Isra'ila,Wanda ya sa dukan al'ummai su girmama mutanensa.
10 Ubangiji ya ce wa Urushalima,“Baƙi ne za su sāke gina garukanki,Sarakunansu kuma za su bauta miki.Na hukunta ki da fushina,Amma yanzu zan nuna miki alheri da jinƙai.
11 Ƙofofinki za su kasance a buɗe dare da rana,Domin sarakunan al'ummai su kawo miki dukiyarsu.
12 Amma al'umman da ba su bauta miki ba,Za a hallakar da su.
13 “Itatuwan fir da irinsuMafi kyau daga jejin Lebanon,Za a kawo su domin a sāke gina ki, ke Urushalima,Domin a ƙawata Haikalina,A darajanta birnina.
14 'Ya'ya maza na waɗanda suka zalunce ki za su zo,Su rusuna, su nuna bangirma.Dukan waɗanda suka raina ki za su yi sujada a ƙafafunki.Za su ce da ke, ‘Birnin Ubangiji,’‘Sihiyona, Birni na Allah Mai Tsarki na Isra'ila.’