1 Aka rufe Yariko ciki da waje, ba mai fita, ba mai shiga saboda Isra'ilawa.
2 Ubangiji ya ce wa Joshuwa, “Duba, na ba da Yariko, da sarkinta, da jarumawanta a hannunka.
3 Kai da dukan mayaƙa za ku zagaya birnin sau ɗaya kowace rana har kwana shida.
4 Sai firistoci bakwai su riƙe ƙahonin raguna a gaban akwatin alkawari. Amma a rana ta bakwai za ku zaga birnin sau bakwai, firistoci su yi ta busar ƙahoni.