9 Kada ka yi wa wawa magana irin ta haziƙai, gama ba zai yaba da maganarka ba.
10 Kada ka kuskura ka kawar da shaidar iyaka, ko ka ƙwace gonar marayu.
11 Ubangiji Mai Iko shi ne kāriyarsu, shi zai yi magana dominsu.
12 Ka mai da hankali ga malaminka, ka koyi dukan abin da kake iyawa.
13 Kada ka bar yaro ba horo, gama ko ka duke shi ba za a kashe shi ba.
14 Lalle ne za ka ceci ransa.
15 Ɗana, idan ka zama mai hikima zan yi murna ƙwarai.