4 Ya faru saboda yawan karuwancinNineba kyakkyawa mai daɗinbaki,Wadda ta ɓad da al'umman duniyada karuwancinta,Ta kuma ɓad da mutane da daɗinbakinta.
5 Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Inagāba da ke,Zan kware fatarinki a idonki,Zan sa al'ummai da mulkoki su dubitsiraicinki.
6 Zan watsa miki ƙazanta,In yi miki wulakanci,In maishe ki abin raini.
7 Dukan waɗanda za su dube kiZa su ja da baya su ce,‘Nineba ta lalace, wa zai yi kukadominta?’A ina zan samo miki waɗanda za suta'azantar da ke?”
8 Kin fi No ne?Wadda take a bakin Nilu,Wadda ruwa ya kewaye ta?Teku ce kagararta.Ruwa ne kuma garunta.
9 Habasha da Masar su ne ƙarfintamarar iyaka,Fut da Libiya su ne kumamataimakanta.
10 Duk da haka an tafi da ita, an kai tacikin bauta.An fyaɗa ƙanananta a ƙasa,An yi kacakaca da su a kowacemararraba.An jefa kuri'a a kan manyanmutanenta,Aka ɗaure dukan manyan mutanentada sarƙoƙi.