32 Idan bisa ga ra'ayin mutum ne, na yi kokawa da namomin jeji a Afisa, mece ce ribata in dai har ba a ta da matattu? “Ba sai mu yi ta ci da sha ba, da yake gobe za mu mutu?”
33 Kada fa a yaudare ku! “Zama da mugaye yakan ɓata halayen kirki.”
34 Ku farka daga magagi, ku kama aikin adalci, ku daina yin zunubi. Waɗansu kam, ba su da sanin Allah. Na faɗi wannan ne don ku kunyata.
35 Watakila wani zai yi tambaya, “Ta yaya ake ta da matattu? Da wace irin kama kuma suke fitowa?”
36 Kai, marar azanci! Abin da ka shuka, ai, ba zai tsiro ba sai ya mutu.
37 Abin da ka shuka kuma, ba shi ne ainihin abin da zai kasance ba, ƙwaya ce ƙawai, ko ta alkama ce, ko kuma, wata iri dabam.
38 Amma Allah yakan ba ta kama, yadda ya nufa, kowace ƙwaya da irin tata kama.