26 Saboda haka, zuciyata ta yi fari, ina farin ciki matuƙa.Ko da yake kuma ni jiki ne, zan zauna ina sa zuciya,
27 Domin ba za ka yar da raina a Hades ba,Ba kuwa za ka yarda Mai Tsarkinka ya ruɓa ba.
28 Kā sanar da ni hanyoyin rai.Za ka cika ni da farin ciki ta zamana a zatinka.’
29 Ya 'yan'uwa, na iya yi muku magana da amincewa a game da kakanmu Dawuda, cewa ya mutu, an binne shi, kabarinsa kuma yana nan gare mu har ya zuwa yau.
30 To, da yake shi annabi ne, ya kuma san Allah ya rantse masa, cewa zai ɗora wani daga cikin zuriya tasa kan kursiyinsa,
31 sai ya hango, ya kuma yi faɗi a kan tashin Almasihu daga matattu, cewa ba za a yashe shi a Hades ba, jikinsa kuwa ba zai ruɓa ba.
32 Yesun nan kam, Allah ya tashe shi daga matattu, mu kuwa duk shaidu ne ga haka.