40 Amma Bitrus ya fitar da su duka waje, ya durƙusa, ya yi addu'a. Ya juya wajen gawar, ya ce, “Tabita, tashi.” Ta buɗe ido, da ta ga Bitrus, ta tashi zaune.
41 Ya kuwa miƙa mata hannu ya tashe ta. Sai ya kira tsarkaka da matan waɗanda mazansu suka mutu ya miƙa musu ita rayayyiya.
42 Labari ya bazu a dukan Yafa, mutane da yawa kuwa suka gaskata da Ubangiji.
43 To, ya zauna kwanaki da yawa a Yafa a gidan wani majemi mai suna Saminu.