12 Ina dai gaya muku, a ran nan, za a fi haƙurce wa Saduma a kan garin nan.”
13 “Kaitonki, Korasinu! Kaitonki, Betsaida! Da mu'ujizan da aka yi a cikinku, su aka yi a Taya da Sidon, da tuni sun tuba, sun zauna sāye da tsumma, suna hurwa da toka.
14 Amma a Ranar Shari'a, za a fi haƙurce wa Taya da Sidon a kanku.
15 Ke kuma Kafarnahum, ɗaukaka ki sama za a yi? A'a, ƙasƙantar da ke za a yi har Hades.
16 “Duk mai sauraronku, ni yake saurare. Mai ƙinku kuma, ni yake ƙi. Duk mai ƙina kuwa, wanda ya aiko ni ne ya ƙi.”
17 Sai kuma saba'in ɗin nan suka komo da farin ciki, suka ce, “Ya Ubangiji, har aljannu ma suna mana biyayya albarkacin sunanka!”
18 Sai ya ce musu, “Na ga Shaiɗan ya faɗo daga sama kamar walƙiya.