23 Sai suka fara tambayar juna ko wane ne a cikinsu zai yi haka.
24 Sai musu ya tashi a tsakaninsu, a kan ko wane ne babbansu.
25 Sai ya ce musu, “Sarakunan al'ummai sukan nuna musu iko, mahukuntansu kuma sukan nema a ce da su, ‘Mataimakan jama'a.’
26 Amma ku kam ba haka ba. Sai dai wanda yake babba a cikinku yă zama kamar ƙarami, shugaba kuwa yă zama kamar mai hidima.
27 Wa ya fi girma? Wanda ya zauna cin abinci, ko kuwa mai hidimar? Ashe, ba wanda ya zauna cin abinci ba ne? Ga shi kuwa, ina a cikinku kamar mai hidima.
28 “Ku ne kuka tsaya gare ni a gwaje-gwajen da na sha.
29 Kamar yadda Ubana ya ba ni mulki, haka, ni ma nake ba ku iko,