15 Wanda yake kan soro kuma kada yă sauko yă shiga gida garin ɗaukar wani abu.
16 Wanda yake gona kuma kada ya koma garin ɗaukar mayafinsa.
17 Kaiton masu juna biyu da masu goyo a wannan lokaci!
18 Ku yi addu'a kada abin nan ya auku da damuna.
19 A lokacin nan za a yi wata matsananciyar wahala, irin wadda ba a taɓa yi ba tun farkon halittar da Allah ya yi, har ya zuwa yanzu, ba kuwa za a ƙara yi ba har abada.
20 Da ba don Ubangiji ya taƙaita kwanakin nan ba, da ba ɗan adam ɗin da zai tsira. Amma sabili da zaɓaɓɓun nan da ya zaɓa, sai ya taƙaita kwanakin.
21 To, a lokacin nan kowa ya ce muku, ‘Kun ga, ga Almasihu nan!’ ko, ‘Kun ga, ga shi can!’ kada ku yarda.