4 Waɗansu kuwa da suka ji haushi, suka ce wa juna, “Mene ne na ɓata mai haka?
5 Gama da ma an sayar da shi fiye da dinari ɗari uku, an ba gajiyayyu!” Sai suka hasala da ita, suna gunaguni.
6 Amma Yesu ya ce, “Ku ƙyale ta. Don me kuke damunta? Ai, alheri ta yi mini, na gaske kuwa.
7 Kullum kuna tare da gajiyayyu, ko yaushe kuma kuke so, kwa iya yi musu alheri, amma ba kullum ne kuke tare da ni ba.
8 Ta yi iyakacin ƙoƙarinta. Ta shafe jikina da mai gabannin jana'izata.
9 Hakika kuwa ina gaya muku, duk inda za a yi bishara a duniya duka, abin da matan nan ta yi, za a riƙa faɗarsa domin tunawa da ita.”
10 Sai Yahuza Iskariyoti, ɗaya daga cikin sha biyun nan, ya je wurin manyan firistoci don ya bashe shi a gare su.