16 to, sai waɗanda suke ƙasar Yahudiya su gudu su shiga duwatsu.
17 Wanda yake soro, kada ya sauko garin ɗaukar wanda yake a gidansa.
18 Wanda yake a gona kuma, kada ya koma garin ɗaukar mayafinsa.
19 Kaiton masu juna biyu da masu goyo a wannan lokaci!
20 Ku yi addu'a kada gudunku ya zo da damuna, ko ran Asabar.
21 A lokacin nan za a yi wata matsananciyar wahala, irin wadda ba a taɓa yi ba tun farkon duniya har ya zuwa yanzu, ba kuwa za a ƙara yi ba har abada.
22 Ba don an taƙaita kwanakin nan ba, da ba ɗan adam ɗin da zai tsira. Amma sabili da zaɓaɓɓun nan za a taƙaita kwanakin.