3 Fāri suka fito zuwa cikin duniya daga cikin hayaƙin nan, aka ba su ikon harbi, irin na kunamin duniya.
4 Aka kuwa hana su cutar ciyayin duniya, ko tsiro, ko kowane itace, sai dai mutanen da ba su da hatimin Allah a goshinsu.
5 Aka kuwa yardar musu su yi musu azaba har wata biyar, amma kada su kashe su, azabarsu kuwa, kamar ta kunama take, in ta harbi mutum.
6 A waɗannan kwanaki kuwa mutane za su nemi mutuwa, amma ba za su same ta ba, za su ƙagauta su mutu, mutuwa kuwa sai ta guje musu.
7 Kamannin fārin nan kuwa kamar dawakai ne da suka ja dāgar yaƙi, a kansu kuma da wani abu kamar kambin zinariya, fuskarsu kuwa kamar ta mutum,
8 gashinsu kamar na mace, haƙorinsu kuma kamar na zaki.
9 Suna saye da sulkuna kamar na ƙarfe, dirin fikafikansu kuwa kamar dirin kekunan doki masu yawa ne suna rugawa fagyan yaƙi,