1 “Kada ku damu. Ku gaskata da Allah, ku kuma gaskata da ni.
2 A gun Ubana akwai wurin zama da yawa. Da ba haka ne ba, da na faɗa muku, domin zan tafi in shirya muku wuri.
3 In kuwa na je na shirya muku wuri, sai in dawo in kai ku wurina, domin inda nake, ku ma ku zama kuna can.
4 Inda za ni kuwa kun san hanya.”