49 Kakannin kakanninku sun ci manna a jeji, amma kuwa sun mutu.
50 Ga Gurasa mai saukowa daga Sama, domin kowa yă ci, kada ya mutu.
51 Ni ne Gurasan rai da ya sauko daga Sama. Kowa ya ci Gurasan nan, zai rayu har abada. Har ma gurasar da zan bayar naman jikina ne, domin duniya ta rayu.”
52 Sai Yahudawa suka ta da husuma a junansu, suna cewa, “Yaya mutumin nan zai iya ba mu naman jikinsa mu ci?”
53 Sai Yesu ya ce musu, “Lalle hakika, ina gaya muku, in ba ku ci naman jikin Ɗan Mutum ba, kuka kuma sha jininsa, ba rai a gare ku.
54 Duk wanda suke cin naman jikina, yake kuma shan jinina, yana da rai madawwami, ni kuwa zan tashe shi a ranar ƙarshe.
55 Domin naman jikina abinci ne na hakika, jinina kuma abin sha ne na hakika.