2 Dawuda ya tashi tare da mutum ɗari shida da suke tare da shi zuwa wurin Akish, ɗan Mawok, Sarkin Gat.
3 Dawuda da mutanensa da iyalansu suka zauna tare da Akish a Gat. Dawuda yana tare da matansa biyu, Ahinowam Bayezreyeliya, da Abigail Bakarmeliya, wadda Nabal mijinta ya mutu.
4 Da Saul ya ga Dawuda ya tsere zuwa Gat, bai ƙara fita nemansa ba.
5 Dawuda ya ce wa Akish, “Idan na sami tagomashi a wurinka, ka ba ni wurin zama daga cikin garuruwanka na karkara domin in zauna a can. Gama me zai sa baranka ya zauna tare da kai cikin birni sarauta?”
6 Sai Akish ya ba shi Ziklag a wannan rana, saboda haka Ziklag ta zama ta sarakunan Yahuza har wa yau.
7 Dawuda ya yi shekara guda da wata huɗu a ƙasar Filistiyawa.
8 Dawuda yakan fita da mutanensa su kai wa Geshurawa, da Girziyawa, da Amalekawa hari. Waɗannan su ne mazaunan ƙasar a dā, tun daga Shur har zuwa ƙasar Masar.