26 Sa'ad da Dawuda ya komo Ziklag, sai ya aika wa abokansa, dattawan Yahuza, da rabo daga cikin ganimar, ya ce, “Ga kyauta dominku, daga cikin ganimar maƙiyan Ubangiji.”
27 Kyautar domin waɗanda suke a Betel, da Ramot ta Negeb, da Yattir,
28 da Arower, da Sifmot, da Eshtemowa,
29 da Rakal, da garuruwa na Yerameyeliyawa, da garuruwa na Ƙan'aniyawa,
30 da Horma, da Ashan, da Atak,
31 da Hebron, da dukan wuraren da Dawuda da mutanensa suka taɓa tafiya.