22 Ya rabu da Ubangiji Allah na kakanninsa, bai bi tafarkin Ubangiji ba.
23 Fādawansa kuwa suka ƙulla masa maƙarƙashiya, suka kashe shi a gidansa.
24 Amma mutanen ƙasar suka kashe waɗannan da suka yi wa sarki Amon maƙarƙashiyar. Sai suka naɗa Yosiya ɗan sarki, ya gāji tsohonsa.
25 Sauran ayyukan da Amon ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuza.
26 Aka binne shi a kabarinsa na gonar Uzza. Ɗansa Yosiya ya gāji sarautarsa.