3 Ubangiji ya ce,“Mutanen Dimashƙu sun ci gaba dayin zunubi.Hakika, zan hukunta su,Don sun zalunci mutanen Gileyad dazalunci mai tsanani.
4 Don haka zan aukar da wuta a kanfādar Sarkin Suriya.Za ta ƙone kagarar Ben-hadad,sarki.
5 Zan ragargaje ƙyamaren ƙofofinbirnin Dimashƙu,In kawar da masu sarautar Bet-edenda na kwarin Awen.Za a kwashe mutanen Suriya ganimazuwa ƙasar Kir.”
6 Ubangiji ya ce,“Mutanen Gaza sun ci gaba da yinzunubi.Hakika, zan hukunta su,Don sun kwashe al'umma duka, sunsayar wa mutanen Edom.
7 Saboda haka zan aukar da wuta akan garun Gaza ta ƙone kagararbirnin.
8 Zan kawar da masu sarautar biranenAshdod da Ashkelon,Zan karɓe sandan mulkin Ekron.Sauran Filistiyawa da suka ragukuma,Za su mutu duka.”
9 Ubangiji ya ce,“Mutanen Taya sun ci gaba da yinzunubi.Hakika, zan hukunta su,Don sun kwashe mutanen sun kaiƙasar Edom.Suka karya yarjejeniyar abuta waddasuka yi.