2 Ko da za su nutsa zuwa lahira,Zan kama su.Ko sun hau Sama,Zan turo su.
3 Ko da za su hau su ɓuya a bisaƙwanƙolin Dutsen Karmel,Zan neme su in cafko su.Ko da za su ɓuya mini a ƙarƙashinteku,Sai in sa dodon ruwa yă yayyage su.
4 Idan kuwa abokan gābansu ne sukakama su,In umarce su su hallaka su datakobi,Tun da na yi ƙudurin ƙare su.”
5 Ubangiji Allah Mai RundunaYa taɓi duniya, ta girgiza.Duk waɗanda suke zaune cikintaSuna baƙin ciki.Duniya duka takan hauTa kuma gangara kamar ruwanKogin Nilu.
6 Ubangiji ya gina al'arshinsa a sama,Ya shimfiɗa samaniya a bisa duniya.Ya sa ruwan teku ya zo,Ya kwarara shi a bisa duniya.Sunansa Ubangiji ne!
7 Ubangiji ya ce, “Jama'ar Isra'ila,Ina yi da ku daidai yadda nake yi daHabashawa.Na fito da Filistiyawa daga Kaftor,Suriyawa kuwa daga Kir,Daidai yadda na fito da ku dagaMasar.
8 Ina dai kallon mulkin nan mai zunubi.Zan hallaka su daga duniya,Amma ba zan hallaka dukan jama'arYakubu ba.