3 Waɗanda suke cewa, ‘Lokacin gina gidaje bai yi kusa ba. Wannan birni tukunya ce mai ɓararraka, mu ne kuwa naman.’
4 Saboda haka ka yi musu annabci marar kyau, ka yi annabci, ya ɗan mutum!”
5 Sa'an nan Ruhun Ubangiji ya sauko a kaina, ya ce mini, “Ka ce, ‘In ji Ubangiji, haka kuke tunani, ku mutanen Isra'ila, gama na san abin da yake cikin zuciyarku.
6 Kun kashe mutane da yawa a wannan birni, har kun cika titunansa da gawawwaki.’
7 “Domin haka Ubangiji Allah ya ce, ‘Gawawwakin da kuka shimfiɗa a cikin birnin su ne naman, birnin kuwa shi ne tukunya mai ɓararraka, amma za a fitar da ku daga cikinsa.
8 Kun tsorata saboda takobi, ni kuwa zan kawo muku takobi,’ in ji Ubangiji Allah.
9 ‘Zan fitar da ku daga cikin birnin, in bashe ku a hannun baƙi, zan hukunta ku.