1 Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce,
2 “Me kuke nufi da faɗar wannan karin magana a kan ƙasar Isra'ila cewa,‘Ubanni sun ci 'ya'yan inabi masu tsami,Hakoran 'ya'ya kuwa sun mutu’?
3 “Ni Ubangiji Allah na ce, hakika, ba za a ƙara faɗar wannan karin magana a Isra'ila ba.
4 Ga shi, dukan rayuka nawa ne, da ran uban da na ɗan, duka nawa ne. Wanda ya yi zunubi shi zai mutu.
5 “Ga irin mutumin da zai rayu, mutumin da yake adali, yana bin shari'a, yana kuma aikata abin da yake daidai,