12 Ta gajiyar da ni a banza,Wutar ba ta fitar da yawan tsatsarta ba.
13 Ya Urushalima, tsatsarki ita ce ƙazantar lalatarki.Da yake na tsabtace ki, ba ki tsabtatu ba,To, ba za ki ƙara yin tsabta ba,Har lokacin da na fashe fushina a kanki.’
14 Ni, Ubangiji na faɗa, zai tabbata gama zan aikata, ba zan fasa ba, ba kuwa zan ƙyale ba, ba kuma zan bari ba. Zan hukunta ki saboda hanyoyinki da ayyukanki, ni Ubangiji Allah na faɗa ”
15 Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce,
16 “Ya ɗan mutum, ga shi, ina gab da ɗauke maka ƙaunatacciyarka farat ɗaya, amma fa, kada ka yi makoki, ko kuka, ko ka zubar da hawaye.
17 Ka yi ajiyar zuciya a hankali, kada ka yi makoki saboda matacciyar. Ka naɗa rawaninka, ka sa takalmanka, kada ka ja amawali, kada kuma ka ci abincin masu makoki.”
18 Sai na yi magana da mutane da safe, da maraice kuwa matata ta rasu. Kashegari da safe, sai na yi kamar yadda aka umarce ni.