9 “Zukatan al'ummai da yawa za su ɓaci, sa'ad da na baza labarin halakarka a ƙasashen da ba ka sani ba.
10 Al'ummai da yawa za su gigice saboda abin da zai same ka, sarakunansu kuma za su yi rawar jiki saboda kai sa'ad da na kaɗa takobi a gabansu. A ranar faɗuwarka za su yi rawar jiki a kowane lokaci, kowa saboda ransa.”
11 Ubangiji Allah ya ce, “Takobin Sarkin Babila zai auko maka.
12 Zan sa ƙarfafan mutane masu bantsoro daga cikin al'ummai su kashe jama'arka da takuba.Za su wofinta girmankan Masar,Su kuma hallaka jama'arta.
13 Zan hallaka dukan dabbobinta da suke bakin ruwa,Ba ƙafar mutum ko ta dabba da za ta ƙara gurɓata ruwa.
14 Zan sa ruwansu ya yi garau,In sa kogunansu su malala kamar mai,Ni Ubangiji Allah na faɗa.
15 Sa'ad da na mai da ƙasar Masar kufai,In raba ƙasar da abin da take cike da shi,Sa'ad da na bugi dukan waɗanda suke cikinta,Daga nan za su sani ni ne Ubangiji.