5 Sai suka warwatsu saboda rashin makiyayin kirki, suka zama abincin namomin jeji.
6 Tumakina sun watse, suna yawo a kan dukan duwatsu da tuddai, sun warwatsu a duniya duka, ba wanda zai nemo su.’
7 “Domin haka, ku ji maganata, ku makiyaya.
8 Ni Ubangiji Allah na ce, ‘Hakika da yake tumakina sun zama ganimar dukan namomin jeji, saboda rashin makiyayin kirki, makiyayana kuma ba su nemo su ba, amma suka yi kiwon kansu, ba su yi kiwon tumakin ba,
9 to, ku makiyaya, sai ku saurara ga maganata.
10 Ga shi, ina gāba da ku, zan nemi tumakina a hannunku. Zan hana ku yin kiwon tumakin, ku kuma ba za ku ƙara yin kiwon kanku ba. Zan ƙwace tumakina daga hannunku, domin kada su ƙara zama abincinku.”’
11 “Ni Ubangiji Allah na ce, ni kaina zan nemi tumakina.