1 Ubangiji ya kuma yi magana da ni, ya ce,
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci Dutsen Seyir, ka yi annabci a kansa.
3 Ka faɗa masa, ni Ubangiji Allah na ce,Ga shi, ina gāba da shi, wato Dutsen Seyir.Zan miƙa hannuna gāba da shi,Zan maishe shi kufai, in lalatar da shi.
4 Zan lalatar da biranensa,In maishe su kufai marar amfani,Sa'an nan zai sani ni ne Ubangiji.