18 A wannan rana Ubangiji ya yi wa Abram alkawari ya ce, “Ga zuriyarka na ba da wannan ƙasa, daga Kogin Masar zuwa babban kogi, wato Kogin Yufiretis ke nan,
19 ƙasar Keniyawa, da Kenizziyawa, da Kadmoniyawa,
20 da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Refayawa,
21 da Amoriyawa, da Kan'aniyawa, da Girgashiyawa, da kuma Yebusiyawa.”