24 Musa kuwa ya saurari maganar surukinsa, ya yi abin da ya ce duka.
25 Sai Musa ya zaɓi isassun mutane daga cikin Isra'ilawa ya naɗa su shugabannin jama'a na dubu dubu, da na ɗari ɗari, da na hamsin hamsin, da na goma goma.
26 Suka yi ta yi wa jama'a duka shari'a kullayaumin, amma matsaloli masu wuya sukan kawo wa Musa, ƙananan kuwa sukan yanke da kansu.
27 Sa'an nan Musa ya sallami surukinsa, ya koma garinsu.