1 Ya Ubangiji, kai ne Allahna, Zan ɗaukaka ka, in yabi sunanka.Ka aikata al'amura masu banmamaki,Ka tafiyar da su da aminci,Wato bisa ga shirin da ka yi tuntuni.
2 Ka mai da birane kufaiKa lalatar da kagaransu,Wuraren da maƙiya suka gina kuwa,An shafe su har abada.
3 Jama'ar al'ummai masu iko za su yabe ka,Za a ji tsoronka a biranen mugayen al'ummai.
4 Matalauta da 'yan ƙaƙa naka yi sun sheƙa zuwa wurinka,Sun sami zaman lafiya a lokatan wahala.Ka ba su mafaka daga hadura,Ka inuwantar da su daga matsanancin zafi.Mugaye sukan tasar musu kamar hadirin ƙanƙara,
5 Kamar fari a ƙeƙasasshiyar ƙasa.Amma kai, ya Ubangiji, ka rufe bakin abokan gābanmu,Ka sa hayaniyar mugaye ta yi tsit,Kamar yadda girgije yake sanyaya zafin rana.
6 A kan Dutsen Sihiyona Ubangiji Mai Runduna zai shirya wa dukan sauran al'umman duniya biki da abinci irin na adaras da ruwan inabi mafi kyau.