22 “Ku juyo wurina a cece ku,Ku mutane ko'ina a duniya!Ni kaɗai ne Allah da yake akwai.
23 Abin da na faɗa gaskiya ne,Ba kuwa zai sāke ba.Ni, a dukkan yadda nake, na yi alkawari mai ƙarfi,Kowa da kowa zai zo ya durƙusa a gabana,Ya yi wa'adin zama mai biyayya a gare ni.
24 “Za su ce ta wurina kaɗaiZa a iya samun nasara da ƙarfi,Amma dukan waɗanda suka raina ni za su sha kunya.
25 Ni Ubangiji, zan kuɓutar da dukan zuriyar Yakubu,Za su kuwa yi yabona.”