18 Sai ta wuce ta yi arewa daura da gefen Bet-araba, daga nan ta gangara zuwa Araba.
19 Ta kuma zarce zuwa arewa daura da gefen Bet-hogla, ta tsaya a arewacin gaɓar Tekun Gishiri a ƙarshen Urdun wajen kudu.
20 Kogin Urdun shi ne iyakar a wajen gabas. Waɗannan su ne iyakokin yankin ƙasar da iyalan kabilar Biliyaminu suka gāda.
21 Biranen iyalan kabilar Biliyaminu ke nan Yariko, da Bet-hogla, da Emekkeziz,
22 da Bet-araba, da Zemarayim, da Betel,
23 da Awwim, da Fara, da Ofra,
24 da Kefar-ammoni, da Ofni, da Geba. Birane goma sha biyu ke nan tare da ƙauyukansu.