16 Mutuwa tana jiran wanda ya ƙi bin hanyar hankali.
17 Sa kai cikin nishaɗi, wato shan ruwan inabi, da cin abinci mai tsada, ba zai bar ka ka tara dukiya ba.
18 Wahalar da mugaye suke so su jawo wa mutanen kirki, za ta koma kansu.
19 Gara ka zauna a hamada, da ka zauna tare da mace mai mita, mai yawan kai ƙara.
20 Mutane masu hikima suna zaune da wadata da nishaɗi, amma wawaye da zarar sun sami kuɗi sukan kashe su nan da nan.
21 Ka yi alheri ka yi aminci, za ka yi tsawon rai waɗansu kuma za su girmama ka, su yi maka abin da yake daidai.
22 Sarkin yaƙi mai wayo yakan ci birnin da jarumawa suke tsaro, ya rushe garun da suke taƙama da shi.